Imamai (A.S) sun kwadaitar da yawa kan yin tawassuli da Kur’ani da waliyyai da sauransu, wanda ya koma wa littattafan imamiyya da hadisansu da littattafan addu’o’insu zai samu wannan ala’mari a wajansu a bayyane yake ta yadda babu wani kokwanto a cikinsa, ga wasu misalai daga ciki:
A- Haris dan Mugira ya rawaito cewa: Na ji Abu Abdullahi (A.S) yana cewa: “Na hana ku wani ya tambayi ubangijinsa wani abu na bukatun duniya har sai ya fara da yabon Allah da kuma salati ga Annabi (S.A.W) sannan sai ya roki Allah bukatunsa” [55].
B- Daga Abu Ja’afar (A.S) ya ce: “Jabirul Ansari ya ce; Na tambayi manzon Allah (S.A.W) me zai ce game da Ali dan Abu Dalib? Sai ya ce: “Wannan shi raina ne, sai na ce: me zaka ce game da Hasan da Husain? Sai ya ce: Su ruhina ne, Fatima babarsu ‘yata ce, duk abin da yake munana mata yana munana mini kuma abin da yake faranta mata yana faranta mini, na shaida har ga Allah ni mai gaba ne ga wanda yake gaba da su, mai aminci ne ga wanda ya aminta da su, ya Jabir, idan kana so ka yi addu’a a amsa maka ka roki Allah da sunayensu, su ne mafi soyuwar sunaye a wajan Allah (S.W.T).
C- Daga annabi (S.A.W) ya ce: “Ya Ubangiji ni ina fuskanta zuwa gareka da Muhammad da alayen Muhammad ina kuma neman kusanci da su zuwa gareka, kuma ina gabatar da su ga bukatuna” [56].
D- Imam Ali (A.S) yana fada a cikin addu’arsa: “Saboda darajar Muhammad da Alayen Muhammad a wajanka, da kuma girmanka mai girma a wajansu ka yi tsira garesu kamar yadda kake ma’abocinsa ka ba ni mafificin abin da ka ba wa masu tambayarka daga bayinka da suka gabata na daga muminai, kuma mafificin abin da kake bayar wa ga wadanda suka ragowa na daga muminai” [57].
E- Imam Husain (A.S) a addu’ar Arfa yana cewa: “Ya Ubangiji ni ina fuskanta zuwa gareka a wannan yammacin da ka halitta, ka girmama, don Muhammad annabinka manzonka, kuma mafificin halittarka” [58].
F- Imam Zainul abidin (A.S) yana fada a addu’arsa don gane da bayyanar watan Ramadan; “Ya Ubangiji ina rokonka don girman wannan wata da kuma girman wanda ya yi bauta a cikinsa -tun farkonsa har zuwa lokacin karewarsa- na daga mala’ika da ka kusantar, ko kuma wani annabi da ka aiko, ko wani bawa na gari da ka zabe shi” [59].
No comments:
Post a Comment