Saturday, 31 May 2014

FALALAR DARIKAR TIJJANIYA

Hadisi Na Ishirin Da Uku

An kar’bo daga Malik, Harisu d’an Asimu Al-sh’ari (Allah ya yarda da shi) yace, “Manzon Allah (tsira d aminci su tabbata Agare Shi) Yace, “Tsarki rabin imani ne, kuma Alhamdulillahi ta kan cika mizani. Kuma Subhaanallahi Walhamdulillahi) Su kan cika ma’auni, ko su cika abindake tsakanin Sama da ‘kasa.
Kuma Sallah Annuri ce;
kuma Sadaqa Dalilice, Hakuri kuma haskene, kuma Alqur’ani Hujja ce Agareka ko akanka.
Dukkan Mutane suna Jijjijifi, wani ya sayarda kansa, wani ya fanshi kansa, wani ya hallaka kansa.”

[Muslim ne Ya Ruwaitoshi]

Hadisi Na Ashirin Da Hud’u

An kar’bo daga Abi Zarrin Al-Gifariyu (Allah ya kara yarda Agareshi) Daga Annabi (Tsira da aminci su kara tabbata Agare Shi) cikin irin Abinda Yake rawaitowa daga Allah, Cewa Allah yace, “Yaku bayina, ha’ki’ka na haramtawa kaina zalunci kima Na Haramta shi Agareku, to kada kuyi zalunci.
Yaa Ku Bayina, dukkanku ‘batattu ne, saidai wanda Na Shiryar.
To ku nemi Shiryata in Shiryar daku.
Yaa ku Bayina dukkanku mayunwata ne, Sai wanda na ciyarm to, ku nemi Ciwayarwata in ciyardaku.
Yaa ku Bayina dukkanku huntaye ne saiwanda Na Tufatar. To ku nemi tufatarwata in tufarta ku.
Yaa ku Bayina ha’ki’ka kuna yin laifi dare da Rana. Ni kuma ina gafarta zunubai baki d’aya, to, ku nemi Gafarata in Gafarta maku.
Yaa ku Bayina Bazaku iya cutar dani ba, Balle ku cuceni.
Kuma baku isa Amfanata Ba, Balle ku Amfane Ni.
Yaa ku Bayina, tundaga farkonku har izuwa na ‘KashanKu.
Da Mutanenku, da Aljaninku, za suyi dai dai da Zuciyar mafi ashararancinku, wannan Bazai rage komi daga Mulki Naba.
Yaa Ku BayiNa da dai tundaga Na Farkonku har izuwa na ‘Karshanku, da mutanen ku da Aljaninku, zaku taru awuri guda, sannan kowannan d’aya ya Rokeni ni kuma in ba kowanne d’aya bukatarsa, wannan Bazai rage komi daga Abinda Na Mallaka Ba.
Sai kamar yadda Allura zata rage in antsoma ta cikin kogi.
Yaa ku Bayina, aiyukankune kurum Nake ‘Kidaya Maku, sannan in Baku Ladansu, To, Wanda duk ya sami Alheri Sai ya godewa Allah. Wanda Kuwa ya sami wanin haka, to, kada ya zargi kowa sai kansa.”

Allahu Akbar. Allah ka bamu dacewa duniya da Lakhira, ameen don Darajar Abba-l Qaasim Sallallahu Alaihi Wa’aalihi Wasahabihi Wa’azwaajihi Wassallam.


Annabin Allah tsira da aminci su ‘kara tabbata Agare Shi Da IyalanSa, Mai Gaskyane Kuma Abin Gasgatawa!


No comments:

Post a Comment