Bismillarrahmanirrahim...Assalatu wassalamu alaika ya Rasulallah
Ya himmat sheikh Ihdirlee pee hazal mahdar...
Zamu gabatarda wani maqaala akan Shehu Tijjani RA da sahabbansa, bawai don mun isa ba. A'a don cika umurni ne
Magana akan akan mazajen darika da sufaye yana kara taraqqie da kusanci koda kuwa za'a mai maita maka abinda kasani ne.... Kalimatan waahidatan turaqqieka ilaa maqaamin lau abadtallah alpu sanaa.....(Magana daya akan bayin Allah zata iya kaika muqaminda koda ka shekara dubu ne kana Ibada bazaka samu wannan taraqqin ba
Allah yasa mudace
Lamarin Auliya'u ana jawo Imani ne akusa ajiye, don ilmi da bincike baisa ayarda dasu sai dai Imani kawai.
Don lamarin yana keta kwakwalwan maiji ko mai karantawa sai dai sami'ina wa ada'ana
Abune wanda yakeda asali amusulunci tun zamanin ma'aiki SAW ba wai saida aka fara karanta Darikaba
Duniya bata zama saida wadannan mazajen, dasu Allah yake kauda musiba, dasu Allah yake bamu ruwan sama, yakke yaye dukkan bala'oi, da za'a kaudasu to da duniya ta tashi gaba daya.
Wadannan mazaje su ake kirada Ahlul Deewan ko kuma Daa'iratu ahlul deewan..wa minhum Qudbul gausi, Autaad, Nuqbaa'u Nujba'u d sauraNsu wanda shehu Tijjani duk ya hade wadannan mazajen
Kuma ana bamu labarinsu Tun Zamanin shugaba SAW. An ANAS RA yace yaji daga wajen ma'aiki saw yace Albudla'u arba'ouna rajulan isnaani wa ishruona bil shaam wa samaniyati ashraa bil iraq...
Ma'aiki saw yace akwai Budla'u su arba'in ne 22 na sham, 18 na Iraq duk wanda ya mutu za'a dauko wani ya maye gurbinsa..idan lokaci yayi wato kiyama za'a janyesu gaba daya adoron kasa. Daganan duniya zata tashi
Munga ashe ba yanzu aka fara ba, kuma duk wanda yake raye arzikinsu yakeci, ya sani ko baisani ba
Wasu sunce akwai IMAMANi su 2, AUTADU 4, BUDLA'u 7, RAJIBIYYUN 30, ABDALU 40 NUJBA'U 70, NUQBA''U 300 AKHYARU 313 sai kuma sauran AULIYA'U
Wadannan duka duniya bata zama saidasu duk wanda ya rasu za'a dauko wani ya maye gurbinsa.
Allah yabamu albarkansu
Alaa ra'asuhum Qudbul Gaus
Kafin mu koro cikin sahabban shehu tijjani masu wadannan darajojin bari mu taba kadan daga tarihin shugaban waliyyan farko da karshe wato maulana shehu Ahmad tijjani RA
Anhaifi shehu a Ainu maad shekara ta. 1150 hijriyya, ma haifinsa ya sakashi makaranta ya hardace kur'ani yana shekara bakwai, sannan yashiga karatun fiqhu har yazama Bahru
Mahaifansa sun rasu rana guda saboda wata annoba da ake kira Daa'oon'
Wannan hasken Rabbaniyyin ita tasa mashi fita don yaje ya haduda mazaje yana da shekara 21.
Y fara isa wani gari da ake kira Abil samgoon, ansayama garin sunan wani waliyyine babba
Anan shehu ya fara samun FATHUL AKBAR iNda yahadu da shugaba SAW a zahiri ba'a barcici ba, ya laqqana masa darikan Tijjaniyya
Yace masa kai danane, kai dana ne na gaskiya, daga yau kabar duk wasu shaihananka, da darikokinsu, da Auradansu. Daga Yau NINE shaihunka nine murabbinka
Anan garin shehu Ya zauna shekara 17 duk duniya saida tabiyoshi nan
Anan yasamu Qudbaniyyatil uzmaa, nan yasamu siddiqiyyq da Fardaniyya da mafatihul kunuz.
Anan yasamu Khatmiyya. Da Qudbaaniyya shamilah
Khatmu.. Mukamine dake tsakanin Nubuwwa da Kudbaniyya. wasu kuma sunce saboda dashi aka cika zirin waliyyai don daga kansa babu wani waliyyi da zaisake zuwa da Darika
Shehu ya tambayi ma'aiki SAW ya rasulallah shin a waliyyai bayan ni waye yakeda mafi daukakan muqami?
Shugaba saw yace shehu Abdulkadir jailani, da ibnul Arabil hatimi
Shehu yace shin sun isonan wannan muqamin? Ma'aiki saw yace na'am Abdulkadir jailani da Ibnul arabi sun shigo, amma Imamu junaidu, Hasnul basari da Imamu Busree sun shigo sun samu kashi daya bisa goma na mukamin sai Tajalli ya rinjayesu basu karaso ba
Abdulkadir jailani ne da Ibnul Arabi suka shigo tsakiya amma suma basukai muntahal maqaam ba.
Wannan shine ma'anan Qudbul makhtoom
Shehu nacewa dukkanin abinda ya kwararo daga zatil aliyyati zai wucene zuwa haqiqatul muhammadiyyati, abinda ya fito daga haqiqatul muhammadiyyati zai wucene zuwa zawatil Anbiyaa, daga wajen anbiya kuwa zai kwararo zuwa zatina ne... Daga garenine ake rabawa dukkanin halittu madadi
Sun sani ko bsau sani ba
Shiyasa wani kudbi a darikan shazilliyya yake cewa. Shi bashaziline amma Allah yabuda masa ya gane wajen shehu Tijjani yake karban madadi
Kowani darika kake shehu Tijjani ke shayarda shehinka, bama kaiba.
Daga nan shehu yabar Abul samgoon zuwa Faas yanada shekara 63 shekarun kakansa SAW
A wannan shekaran aka haifi sheikh ummarul footee... A fouta toro
Ya shiga fass ranar laraba... Wafil muharrami gadaa gaus rashaad.. Halifatan anil muhaiminul majid..
Inji ibnul babal alawi.
A daren lahadine na. 12 gawatan muharram. Aka tabbatarda shehu shine khalifatullahi pee ardihi wa samaa'ihi
A watan safar kuma 18 gawata me kira ya kirashi zuwa filin arfa ya tafi tareda sahibinsa syd Aliyu harazimi, akayi abinda akayi acan
Daganan ne yazama kudbul makhtoom.. Saboda haka shehu ke cewa munada muqami wanda babu wanda yasanshi sai Allah, da zamu bude da manyan rijalai sun karyatamu, wasuma kafirtamu zasuyi
Daganan ya halifantarda syd Aliyu harazimi muqamul hidmati wato Qudbaniyya
Sayyidu aliyul harazimi shi yafara zama a wannan muqamin, dagashi sai syd Muhammad tunussee, ya kwana 7, kwana bakwai kawai yayi amma aka ganshi ya shiga gari yana ihu yana cewa bazan iya daukaba, bazan iya daukaba, ahaka harya mutu
Bayanshi sai babban namiji wato syd Aliyul Tamasini, dominshi saida ya shekara 30.
No comments:
Post a Comment