Saturday, 31 May 2014

MALAMI DA MALUNTA A KASAR HAUSA


1.0 Gabatarwa
A cikin wannan makala za mu yi bayani filla-filla a kan abin da ake nufi da malami, da rabe-raben aikin malami da kuma lakuba da ake kiran malami da su a kasar Hausa. Manufar wannan makala ita ce nuna muhimmanci da kuma martabar da malami yake da shi ko ita a da, da yanzu, da kuma nuna yadda canje-canje na zamani suka shafi matsayin malami da sana'ar malanta a kasar Hausa1.

2.0 Ma'anar Malami
Abin da muke nufi da malami a wannan makala shi ne masanin Alkur'ani Mai girma, da ilmin Furu'a, da shari'ar Musulunci, da na harshen Larabci. Almajiri kuwa, shi ne mai yawon neman ilmi ko sadaka2. A kasar Hausa malami shi ne wanda yake da ilmin addinin Musulunci kuma yake karantar da shi. In malami ne da ilmin addinin Musulunci amma ba ya karantarwa, ya kuma kama sana'a, ba a lissafa shi cikin sahun malamai. Haka nan kuma, in malami ya shagala da neman abin duniya, mutane ba su dubansa da mutunci domin za su dauka ya ci amanar ilmi ke nan. Wani lokaci akan lissafa shi cikin masu bidi'a.

3.0 Sunayen Malamai
A kasar Hausa akwai sunayen iri-iri da ake kiran malami da su. Akwai malamin sunna,3 da malamin bidi'a,4 da malamin tsibbu,5 da sarkin malamai, da malamin malamai, da shehun malami, da kuma waliyyin malami. Ga takaitaccen bayani a kan kowannensu.

3.1 Malamin Sunna:
Shi ne malamin da ke da ilmin addinin Musulunci gwargwado, kuma yana karantar da shi ga jama'a. bugu da kari, yana da takawa da natsuwa da tsentseni da gudun duniya na inna naha. Kuma ga shi ba shi da tsoron fadin gaskiya a kan komai da kowa. Haka kuma, bai damu da fushin wani ba a wajen fadin gaskiya. Ire-iren wadannan na da wuyar samuwa. Amma ana samunsu domin bayin Allah nagari ba su karewa.

3.2 Malamin Bidi'a
Shi ne wanda yake da ilmin addinin Musulunci, kuma yana karantar da shi ga mutane, amma yana da kwadayin abin da ke hannun mutane da kuma tsananin son dukiya a zuciyarsa.

3.3 Malamin Tsibbu
In malami ya shagala da ba maras lafiya magani ta hanyar amfani da ayoyin Alkur'ani Mai Girma, da yin layu, kuma yana bugun kasa don ya fada wa mutane alherin da za su samu ko cutar da za ta same su, to akan kira shi malamin tsibbu6.

3.4 Sarkin Malamai
A wasu wurare cikin kasar Hausa, in malamai na da yawa, sarkin garin yakan nada musu shugaba. Shugaban malamai a gari ko a kasa, shi ne sarkin malamai wanda yake ba dole ne ya zama ya fi dukkan malaman garin ilmi ba. A halin yanzu akwai sarkin malamai a Sakkwato.

3.5 Malamin Malamai
Idan malami ya shahara kwarai da gaske a kan ilmin addinin Musulunci, har wasu malamai da almajirai na zuwa daga nesa saboda neman ilmin a wurinsa, akan kira wannan malami da lakabin 'Malamin Malamai'. Hausawa sun sami wannan suna ne daga Larabawa da ke kiran wasu malamansu da lakabin “Shaykh al-shuyukhi”. Da “Al'allamat”, da faridu dahrihi”. Ana nufi da wadannan lakubba babban malami wanda babu na biyunsa a kasarsa ko a zamaninsa.

3.6 Shehun Malami
Shi ne malamin da ya yi zurfi a cikin ilmin Sufanci da darikun waliyyai magabata. Haka nan kuma, akan kira irin wannan malami da sunan “Malamin darika”. Wani lokaci in malami ya tsufa kwarai har ya ba shekara sittin baya, akan kira shi “Shehun Malami”7.

3.7 Waliyyi
Wani lokaci akan samu malami mai tsananin tsoron Allah da natsuwa da gudun duniya da yawan ibada da ilhami. Har ma in ya yi magana a kan wani abu da zai auku, sai abin ya auku yadda ya ba da labari. Malamai masu irin wadannan siffofi da muka zana, akan yada cewa su waliyyai ne. Abin da ake nufi da waliyyai, shi ne bayin Allah da Allah ke so, wadanda za su shiga Aljanna. Hausawa sun dauka cewa waliyyi yana da ikon nuna karama yadda ya so, kuma a lokacin da ya so. Sun yi imani cewa, waliyyi na iya abin da sauran mutane ba za su iya yi ba, kamar tafiya a kan ruwa ba tare da jirgi ba, ko tafiya wuri mai nisa cikin lokaci kankane, ko kuma rayuwa wata da watanni ba tare da ci da sha ba. Da kuma makamantansu 8.
A kasar Hausa akwai malamai da yawa wadanda suka shahara da walitaka. Mutane da yawa sun dauke su waliyyan Allah ne wadanda za su shiga Aljanna kai-tsaye, ba tare da wahala ba. Daga cikinsu akwai Wali Danmarina,9 da Wali Danmasani,10 da Mujaddadi Shehu Usmanu Danfodiyo11. Haka nan kuma akwai karamomin iri-iri da aka danganta ga kowannensu.

3.8 Malamin Allo
Malamin da ke karantar da yara Alkur'ani Mai Girma da allo, shi ne ake kira 'Malamin allo'. Sau da yawa malamin allo almajiri ne. Bayan yara sun tashi daga makarantarsa, yakan tafi wajen babban malami wanda ya fi shi sani don daukar ilmi.

3.9 Malamin Zaure 12
Akan kira malamin allo 'Malamin zaure' in ya kasance yana karantar da yara karatun Alkur'ani da allo, kuma yana karantar da manyan littattafai kamar su Lahalari da Ishmawi da Izziyya da Risala.

3.10 Alaramma
Wannan shi ne lakabin malami da ke da sanin Alkur'ani sosai. Asalin kalmar Larabci ce (Allahu Yarhamu ka). Ma'anarta, 'Allah shi rahamshe ka'. Kafin a kira malami alaramma, sai ya haddace Alkur'ani Mai Girma, kuma yana iya rubuta shi da ka, hakanan kuma yana iya bayanin tsari da rabe-raben surorin Alkur'ani da ka.

3.11 Malamin Gafaka
Wannan shi ne malami wanda yake yawo da almajiransa daga wani wuri zuwa wani wuri. Ba shi da sana'ar neman abinci ban da karantar da yara Alkur'ani Mai Girma. Ya dogara ne a kan sadakar da mutane kan ba shi da kuma hidima da almajiransa ke yi masa.

3.12 Ustazu 13
Yanzu Hausawa kan kira mutum 'Ustazu' in sun ga alama cewa yana yin shiga irin ta malamai, kuma yana da ra'ayin rikau game da sha'anin addini, ko da kuwa ba shi da isasshen ilmin Addinin Musulunci. Haka kuma akan kira mutum Ustazu in malami ne shi, amma ba ya son darika, kuma ba ruwansa da ilmin Sufanci. Wani lokaci akan kira irin wannan malami 'Malamin Izala'.

4.0 Aikin Malami
4.1 Karantarwa
Babban aikin malami a kasar Hausa shi ne karantar da mutane addinin Musulunci, Alhakinsa ne ya karantar da mutane Alkur'ani Mai Girma, da Furu'a, da dukkan abin da ya shafi Shari'a. Karantarwa ce ke sa wani lokaci malami ya shahara. Sai sunansa ya kai wurare da dama, kuma almajirai su yi ta zuwa wajensa daga kusa da nesa domin neman ilmi da albarka a wajensa.14

4.2 Wa'azi 15
Wa'azi shi ne kiran mutane zuwa hanyar Allah. Manufar wa'azi shi ne shiryar da mutane yadda ake ibada da zaman lafiya tare da jama'a. Mai wa'azi yakan yi bayanin yadda ake Alwala, da Sallah, da Azumi, da Zakka, da aikin Hajji. Malami mai wa'azi yakan yi albishir ga masu saurarensa. Yakan yi musu albishir da shiga Aljanna in aka yi aikin kwarai a nan duniya. Haka kuma yakan yi gargadi a kan wutar lahira da azabarta wadda Allah Ya tanada wa Fir'auna, da Karuna, da Hamana, da wadanda suka yi aikin assha irin nasu.
A majalisar wa'azi, malami yakan gamu da wautar mutane daban-daban. Wasu sukan halarci wurin wa'azi saboda su kure malamin da tambaya. Wasu kuma sukan zo domin sukan halayen malami mai wa'azi don mutane su watse daga wurin wa'azinsa.16 Wani lokaci akan sami wasu mutane da ke surutu da izgili lokacin da ake wa'azi. Su ba su sauraron wa'azin da ake yi, kuma ba su barin masu saurare su ji abin da ake fadi. Mujaddadi Shehu Usmanu Danfodiyo ya gamu da ire-iren wadannan abubuwa da muka zana yayin da yake wa'azi a kasar Hausa a cikin karni na goma sha tara na Miladiyya17.


4.3 Talifi
Burin malami shi ne dalibansa su gane abin da yake koya musu. In malami ya gane dalibansa na fama da rashin gane wani littafi saboda tsaurinsa, sai malamin ya yi wa dalibansa sharhi ko bayanin littafin a rubuce don saukin fahimta18.
Saboda haka ne Shehu Usmanu da mukarrabansa suka yi talifi da yawa a kan fannonin addinin Musulunci daban-daban ga jama'ar Musulmi don su gane addini cikin sauki. Kuma ya yi kira ga malaman kowane zamani su yi talifi ga jama'arsu saboda su suka fi sanin matsalolin zamaninsu da na mutanensu19.
Shehu Usmanu ya nuna misali da yin talifi fiye da dari. Haka nan kuma kaninsa Malam Abdullahi Ibn Fodiyo, da kuma dansa Sarkin Musulmi, Muhammadu Bello 20.

4.4 Alkalanci
Babu wanda ya cancanta ya zama alkali sai malami mai tsoron Allah, kuma adali. A kasar Hausa, in aka ga malami yana da takawa da ilmin Shari'a mai zurfi, ga shi kuma adali, akan nada shi alkali. Kafin zuwan Turawan Mulkin Mallaka kasar Hausa 21, mafi yawan sarakunanta malamai ne. Kuma su ne ke alkalanci ga jama'arsu. In aiki ya yi wa sarki yawa ne yake nada wani malami alkali. Zuwan Turawa kasar Hausa ya sa alkalai cikin halin kaka-nika-yi. In sun yanke hukunci a bisa Shari'ar Musulunci, sai Bature ko dan korensa ya soke in ya ga dama. Wannan ya sa yanzu malamai masu tsoron Allah suna guje wa aikin Shari'a. Abin ya kai ga lahaula, har jahilai ne ma ake nadawa alkalai a wasu kotuna yanzu.


4.5 Limanci
Limancin Sallah yana daya daga cikin muhimman ayyukan malami. A kasar Hausa akwai limamai biyu “Limamin Khamsu Salawatu” (Salloli Biyar), da kuma “Limamin Masallacin Jumu'a”. Na farko suna da yawa. Kusan akwai su a kowace unguwa. Na biyu kuwa, sarkin gari, ko hakimi, ko mai unguwa tare da yardar wasu malamai ne ke nada shi. Har ila yau, malami ne ke limancin sallar gawa, da ta Idi, da ta rokon ruwa da ta husufin rana da wata.

4.6 Shawara
Malami mai basira shi ne sarki ke neman shawararsa in yana da matsala. Shi ne kuma babban abokin shawara ga sarki. Saboda haka, a cikin majalisar sarakunan kasar Hausa, akan sami akalla malami guda wanda zai dinga ba da shawara ga sarki a kan al'amuran yau da kullum, da kuma wadanda suka shafi addinin Musulunci.
Wani lokaci akan kira malamai masu ba sarki shawara da “Malaman Fada”. Amma su malaman sun fi son a kira su da sarautar da sarki ya fi ba malamai; wadda ita ce: Waziri, da danmasani, da Sarkin Malamai, da dai makamantansu.

4.7 Rabon Gado
Rabon gado wani babi ne mai wuyar sani a cikin ilmin Furu'a. Amma ga malami mai zurfin sani, abu ne mai sauki. Saboda haka, in magada suka rasa sanin yadda za su raba dukiyar gado a tsakaninsu, sukan nufi malam don ya ilmantar da su a kai, kuma ya raba musu dukiyar gadon, ko kuma a kai wurin alkali.

4.8 Daurin Aure Da Radin Suna Da Saukar Alkuri'ani
In za a daura aure, akan gayyaci malamai su albarkaci taron, da kulla auren, da kuma yin addu'a. Galibi, malamai kan yi wa waliyyansu nasiha a kan hakkokin ma'aura. Kuma sukan roki Allah Ya albarkaci zamansu na aure, da zuriya mai albarka, da 'ya'ya managarta, da kuma yalwar arziki da zaman lafiya. Haka kuma suke yi in an gayyace su wurin radin suna.

4.9 Biyan Bukata
A kasar Hausa, mutane da yawa sun dauka cewa malami yana da tsarkin zuciya da imani fiye da sauran mutane. Saboda haka, sun yi imani Allah ya fi sauraron rokonsa fiye da na wani.
In Allah Ya ba malami ijaba, sai ka ga attajirai, da saraki, da talakawa, da masu sana'o'i iri-iri maza da mata na ta tururuwa zuwa gidansa saboda neman biyan bukata. Wasu tsari suke nema da zai kare su daga sharrin bil'adama da sauran halittun Ubangiji. Matan aure kan so malam ya rokar musu Allah Ya ba su zuriya mai albarka in ba su da da, ko kuma kada Allah Ya ba mazansu ikon yi musu kishiya. Sarakuna sukan nemi addu'ar malami, Allah Ya kare su da jama'arsu daga sharrin abokan gabansu, ya kuma ba su lafiya da zaman lafiya da damina mai albarka. Attajiri yakan je wajen malami don neman tsari da karin arziki. A takaice dai, ba jinsin mutane da ba su zuwa wajen malami saboda wata bukata.

5.0 Matsayin Malami A Yau
A yau an samu sauyi sosai game da aikace-aikacen malami a kasar Hausa. Saboda huldar al'ummar Hausawa da Turawan Mulkin Mallaka da wasu kabilu daban-daban a cikin kasarsu da wajenta. Matsayin malami ya bambanta da yadda aka sani da can karni biyu da suka wuce.
A halin yanzu, an fara samun malamai a kasar Hausa masu ba da taimako ga 'yan fashi da barayi, da 'yan daudu da karuwai. Haka nan kuma, yanzu ana samun malamai masu zaman bauta ga masu hannu-da-shuni. Sai mai hali ya gina katon gida da masallaci da makaranta da gidan yara. Sai ya sa malami a gidan yara yana ciyar da shi da iyalansa. Shi kuma malamin yana karantar da yaran mai gida da matansa ilmin addini, kuma yana ba da sallah a cikin masallacin gida. In mai gidan mai hali ne sosai, sai ya biya wa malamin kujerar Hajji. Amma abin ban haushi shi ne, ranar da malamin ya yi wa mai gidan laifi, sai mai gidan ya kore shi daga gidansa korar kare.

6.0 Kammalawa
A cikin wannan makala mun yi bayani a kan malami a kasar Hausa. Mun tattauna abubuwa da yawa a kan sunayensa, da aikace-aikacensa, da kuma matsayinsa a cikin jama'a a da, da kuma yanzu. Babu shakka, wanda ya yi tsokaci a kan abubuwan da muka fada, zai gane cewa, ba karamin matsayi ne malami yake a cikin al'ummar Hausawa ba. Saboda muhimmancinsa, an dauke shi kamar gishiri ne ga miya. Da shi jama'a ke zama salihai. In kuma sun lalace (Allah Ya kiyaye). Jama'a sun shiga uku. Abin farin ciki kuma shi ne ba ga mutane kawai malami ke da daraja ba. Malamai masu aiki da ilminsu na da daraja a wajen Mahaliccinsu Allah har ma ya ce: “Masu tsoron Allah cikin bayanisa, su ne malamai”22. A wajen Manzo Allah ma, malamai masu daraja ne har ma ya ce game da su: “Malamai su ne magadan Annabawa”23. A kasar Hausa kuwa, in an kira sarki, sai a kira limaminsa.
Ina fata malamanmu za su ci gaba da yi mana jagora zuwa ga tafarkin tsira. Allah ya sa, amin.

TUSHEN BAYANI
1. Ka dubi The Hausa Factor in West Afircan History Mahadi Adamu, Ahmadu Bello University      Pres Zaira, 1978, saboda karin bayani a kan kasar Hausa da iyakarta.
2. Ka karanta: Islam in Nigeria A.R Doi, saboda karin bayani a kan yaduwar Musulunci a kasar Hausa, shafi na 307-333.
3. Ma'anar kalmar “Sunna” na da yawa. Ka dubi littafin da ake kira Al-Sunnat Wa Ma'anatuha Fil Islam, na likita Mustafa Alsiba'i, shafi na 45-74.
4. Ka karanta rabe-raben bidi'a a cikin Ihya'u Sunna na Shehu Usmanu Danfodiyo, shafi na 22-28, bugu na Misra wanda Sardauna Sir. Ahmadu Bello ya dauki nauyin bugawa, 1963 a Misra.
5. Asalin kalmar “Tsibbu” daga Larabci ne “Tibbu” (magani).
6. Wani lokaci akan kira malamin tsibbu, “Gobe-da-nisa” in yana ba da maganin kisan mutum.
7. Dubi kamus da ake kira, Al-Munjid Fil Lugati Wal A’lami, bugu na 21, wanda aka yi a Lebanon a 1973, shafi na 41.
8. Ka dubi Lamma Balagtu” na Shehu Usmanu Danfodiyo, za ka ga irin karamomi da Allah Ya ba shi a shafi na 14-17. bugu na madaba'ar Amiriya da ke kano.
9. Akwai labarin tarihin wali Danmarina a cikin littafin Ibrahim Yaro Yahaya Hausa A Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin Hausa NNPC Zaria, 1988, shafi na 36.
10. Ka dubi Hausa A Rubuce, shafi na 37.
11. Ka dubi Hausa A Rubuce, shafi na 49.
12. Ka dubi makalar Mahmud Inuwa mai take “Malaman Zaure: A Legacy of Western Colonial Education System In Northern Nigeria”, Shafi na 13.
13. Akwai ma'anarsa ta asali a cikin “Munjid”, shafi na 10. Shehun malami mai zurfin ilmi ne ake nufi da shi, kamar su Shehu Abdullahi Danfodiyo dai malam Jibirilu dan Umar, malamin Shehu Usmanu Danfodiyo.
14. Dubi tarihin Shehu Usmanu Danfodiyo wanda Ibrahim Imam ya rubuta.
15. Domin karin bayani ka dubi Nasiha Da Wa'azi A Cikin Musulunci, tailfin Habib Alhassan.
16. Domin karin bayani ka dubi Infakul Maisuri, wanda Muhammadu Bello ya rubuta, shafi na 91-94.
17. Ka dubi Infakul Maisuri wanda Alhaji Dan'ige ya dauki nauyin bugawa, shafi na 91.
18. Shehu Usmanu ya yi wa jama'a nasiha da su yi karatun littafinsa da na sauran malamai. Ka dubi karshen littafinsa da ake kira Najmul Ikhwani.
19. Ka dubi Najmul Ikhwani, shafi na 43.
20. In kana neman sunayen littattafansa ka dubi makalar Bashir Osman Ahmad, mai take Al-Ishamul Fikri Li Ulama'i Sakkwato.
21. Saboda karin bayani ka dubi Islamic Law in Nigeria na Sayyid Khalid Rashed, lagos, Islamic Publications Bureau, 1986, shafi na 75-80.

ZIKIRIN DARIKAR TIJJANIYA

ZIKIRIN DARIKAR TIJJANIYA

Abin da ya zama Lazim a Darikar Tijjaniyya Guda uku ne:
1) Wurudin Safe da Yamma.
2) Sai Wazifa a Wunin ko da Dare.
3) Sai Zikirin Juma'a.

To mene ne Wurudin?
Wurudin kashi uku ne:
1) Itigfari 100
2) Salatul-fatih 100
3) Hailala 100

To mene ne Wazifa?
Wazifz abubuwa Hudu ne suka hada Wazifa:
1) Istigfari 30
2) Salatul-fati 50
3) Hailala 100
4) Jauharatul-kamali 12
Gawanda ya Haddace ta kuma ya zaune a gida ba matafiyi ba ko wanda yake kan Dabba ko abin hawa, to sai ya karanta Salatul-fatih 20 kawai ta wadatar banta Jauharatil-kamalin.

ZIKIRIN DARIKAR TIJJANIYA

ZIKIRIN DARIKAR TIJJANIYA

Abin da ya zama Lazim a Darikar Tijjaniyya Guda uku ne:
1) Wurudin Safe da Yamma.
2) Sai Wazifa a Wunin ko da Dare.
3) Sai Zikirin Juma'a.

To mene ne Wurudin?
Wurudin kashi uku ne:
1) Itigfari 100
2) Salatul-fatih 100
3) Hailala 100

To mene ne Wazifa?
Wazifz abubuwa Hudu ne suka hada Wazifa:
1) Istigfari 30
2) Salatul-fati 50
3) Hailala 100
4) Jauharatul-kamali 12
Gawanda ya Haddace ta kuma ya zaune a gida ba matafiyi ba ko wanda yake kan Dabba ko abin hawa, to sai ya karanta Salatul-fatih 20 kawai ta wadatar banta Jauharatil-kamalin.

FALALAR DARIKAR TIJJANIYA

Hadisi Na Ishirin Da Uku

An kar’bo daga Malik, Harisu d’an Asimu Al-sh’ari (Allah ya yarda da shi) yace, “Manzon Allah (tsira d aminci su tabbata Agare Shi) Yace, “Tsarki rabin imani ne, kuma Alhamdulillahi ta kan cika mizani. Kuma Subhaanallahi Walhamdulillahi) Su kan cika ma’auni, ko su cika abindake tsakanin Sama da ‘kasa.
Kuma Sallah Annuri ce;
kuma Sadaqa Dalilice, Hakuri kuma haskene, kuma Alqur’ani Hujja ce Agareka ko akanka.
Dukkan Mutane suna Jijjijifi, wani ya sayarda kansa, wani ya fanshi kansa, wani ya hallaka kansa.”

[Muslim ne Ya Ruwaitoshi]

Hadisi Na Ashirin Da Hud’u

An kar’bo daga Abi Zarrin Al-Gifariyu (Allah ya kara yarda Agareshi) Daga Annabi (Tsira da aminci su kara tabbata Agare Shi) cikin irin Abinda Yake rawaitowa daga Allah, Cewa Allah yace, “Yaku bayina, ha’ki’ka na haramtawa kaina zalunci kima Na Haramta shi Agareku, to kada kuyi zalunci.
Yaa Ku Bayina, dukkanku ‘batattu ne, saidai wanda Na Shiryar.
To ku nemi Shiryata in Shiryar daku.
Yaa ku Bayina dukkanku mayunwata ne, Sai wanda na ciyarm to, ku nemi Ciwayarwata in ciyardaku.
Yaa ku Bayina dukkanku huntaye ne saiwanda Na Tufatar. To ku nemi tufatarwata in tufarta ku.
Yaa ku Bayina ha’ki’ka kuna yin laifi dare da Rana. Ni kuma ina gafarta zunubai baki d’aya, to, ku nemi Gafarata in Gafarta maku.
Yaa ku Bayina Bazaku iya cutar dani ba, Balle ku cuceni.
Kuma baku isa Amfanata Ba, Balle ku Amfane Ni.
Yaa ku Bayina, tundaga farkonku har izuwa na ‘KashanKu.
Da Mutanenku, da Aljaninku, za suyi dai dai da Zuciyar mafi ashararancinku, wannan Bazai rage komi daga Mulki Naba.
Yaa Ku BayiNa da dai tundaga Na Farkonku har izuwa na ‘Karshanku, da mutanen ku da Aljaninku, zaku taru awuri guda, sannan kowannan d’aya ya Rokeni ni kuma in ba kowanne d’aya bukatarsa, wannan Bazai rage komi daga Abinda Na Mallaka Ba.
Sai kamar yadda Allura zata rage in antsoma ta cikin kogi.
Yaa ku Bayina, aiyukankune kurum Nake ‘Kidaya Maku, sannan in Baku Ladansu, To, Wanda duk ya sami Alheri Sai ya godewa Allah. Wanda Kuwa ya sami wanin haka, to, kada ya zargi kowa sai kansa.”

Allahu Akbar. Allah ka bamu dacewa duniya da Lakhira, ameen don Darajar Abba-l Qaasim Sallallahu Alaihi Wa’aalihi Wasahabihi Wa’azwaajihi Wassallam.


Annabin Allah tsira da aminci su ‘kara tabbata Agare Shi Da IyalanSa, Mai Gaskyane Kuma Abin Gasgatawa!


TARIHIN SHEHU TIJJANI RTA DA SAHABBANSA

TARIHIN SHEHU TIJJANI RTA DA SAHABBANSA

Bismillarrahmanirrahim...Assalatu wassalamu alaika ya Rasulallah
Ya himmat sheikh Ihdirlee pee hazal mahdar...
Zamu gabatarda wani maqaala akan Shehu Tijjani RA da sahabbansa, bawai don mun isa ba. A'a don cika umurni ne
Magana akan akan mazajen darika da sufaye yana kara taraqqie da kusanci koda kuwa za'a mai maita maka abinda kasani ne.... Kalimatan waahidatan turaqqieka ilaa maqaamin lau abadtallah alpu sanaa.....(Magana daya akan bayin Allah zata iya kaika muqaminda koda ka shekara dubu ne kana Ibada bazaka samu wannan taraqqin ba
Allah yasa mudace
Lamarin Auliya'u ana jawo Imani ne akusa ajiye, don ilmi da bincike baisa ayarda dasu sai dai Imani kawai.
Don lamarin yana keta kwakwalwan maiji ko mai karantawa sai dai sami'ina wa ada'ana
Abune wanda yakeda asali amusulunci tun zamanin ma'aiki SAW ba wai saida aka fara karanta Darikaba
Duniya bata zama saida wadannan mazajen, dasu Allah yake kauda musiba, dasu Allah yake bamu ruwan sama, yakke yaye dukkan bala'oi, da za'a kaudasu to da duniya ta tashi gaba daya.

Wadannan mazaje su ake kirada Ahlul Deewan ko kuma Daa'iratu ahlul deewan..wa minhum Qudbul gausi, Autaad, Nuqbaa'u Nujba'u d sauraNsu wanda shehu Tijjani duk ya hade wadannan mazajen
Kuma ana bamu labarinsu Tun Zamanin shugaba SAW. An ANAS RA yace yaji daga wajen ma'aiki saw yace Albudla'u arba'ouna rajulan isnaani wa ishruona bil shaam wa samaniyati ashraa bil iraq...
Ma'aiki saw yace akwai Budla'u su arba'in ne 22 na sham, 18 na Iraq duk wanda ya mutu za'a dauko wani ya maye gurbinsa..idan lokaci yayi wato kiyama za'a janyesu gaba daya adoron kasa. Daganan duniya zata tashi
Munga ashe ba yanzu aka fara ba, kuma duk wanda yake raye arzikinsu yakeci, ya sani ko baisani ba
Wasu sunce akwai IMAMANi su 2, AUTADU 4, BUDLA'u 7, RAJIBIYYUN 30, ABDALU 40 NUJBA'U 70, NUQBA''U 300 AKHYARU 313 sai kuma sauran AULIYA'U
Wadannan duka duniya bata zama saidasu duk wanda ya rasu za'a dauko wani ya maye gurbinsa.
Allah yabamu albarkansu
Alaa ra'asuhum Qudbul Gaus
Kafin mu koro cikin sahabban shehu tijjani masu wadannan darajojin bari mu taba kadan daga tarihin shugaban waliyyan farko da karshe wato maulana shehu Ahmad tijjani RA
Anhaifi shehu a Ainu maad shekara ta. 1150 hijriyya, ma haifinsa ya sakashi makaranta ya hardace kur'ani yana shekara bakwai, sannan yashiga karatun fiqhu har yazama Bahru
Mahaifansa sun rasu rana guda saboda wata annoba da ake kira Daa'oon'
Wannan hasken Rabbaniyyin ita tasa mashi fita don yaje ya haduda mazaje yana da shekara 21.
Y fara isa wani gari da ake kira Abil samgoon, ansayama garin sunan wani waliyyine babba
Anan shehu ya fara samun FATHUL AKBAR iNda yahadu da shugaba SAW a zahiri ba'a barcici ba, ya laqqana masa darikan Tijjaniyya
Yace masa kai danane, kai dana ne na gaskiya, daga yau kabar duk wasu shaihananka, da darikokinsu, da Auradansu. Daga Yau NINE shaihunka nine murabbinka
Anan garin shehu Ya zauna shekara 17 duk duniya saida tabiyoshi nan
Anan yasamu Qudbaniyyatil uzmaa, nan yasamu siddiqiyyq da Fardaniyya da mafatihul kunuz.

Anan yasamu Khatmiyya. Da Qudbaaniyya shamilah
Khatmu.. Mukamine dake tsakanin Nubuwwa da Kudbaniyya. wasu kuma sunce saboda dashi aka cika zirin waliyyai don daga kansa babu wani waliyyi da zaisake zuwa da Darika
Shehu ya tambayi ma'aiki SAW ya rasulallah shin a waliyyai bayan ni waye yakeda mafi daukakan muqami?
Shugaba saw yace shehu Abdulkadir jailani, da ibnul Arabil hatimi
Shehu yace shin sun isonan wannan muqamin? Ma'aiki saw yace na'am Abdulkadir jailani da Ibnul arabi sun shigo, amma Imamu junaidu, Hasnul basari da Imamu Busree sun shigo sun samu kashi daya bisa goma na mukamin sai Tajalli ya rinjayesu basu karaso ba
Abdulkadir jailani ne da Ibnul Arabi suka shigo tsakiya amma suma basukai muntahal maqaam ba.

Wannan shine ma'anan Qudbul makhtoom
Shehu nacewa dukkanin abinda ya kwararo daga zatil aliyyati zai wucene zuwa haqiqatul muhammadiyyati, abinda ya fito daga haqiqatul muhammadiyyati zai wucene zuwa zawatil Anbiyaa, daga wajen anbiya kuwa zai kwararo zuwa zatina ne... Daga garenine ake rabawa dukkanin halittu madadi
Sun sani ko bsau sani ba
Shiyasa wani kudbi a darikan shazilliyya yake cewa. Shi bashaziline amma Allah yabuda masa ya gane wajen shehu Tijjani yake karban madadi
Kowani darika kake shehu Tijjani ke shayarda shehinka, bama kaiba.
Daga nan shehu yabar Abul samgoon zuwa Faas yanada shekara 63 shekarun kakansa SAW
A wannan shekaran aka haifi sheikh ummarul footee... A fouta toro
Ya shiga fass ranar laraba... Wafil muharrami gadaa gaus rashaad.. Halifatan anil muhaiminul majid..
Inji ibnul babal alawi.

A daren lahadine na. 12 gawatan muharram. Aka tabbatarda shehu shine khalifatullahi pee ardihi wa samaa'ihi
A watan safar kuma 18 gawata me kira ya kirashi zuwa filin arfa ya tafi tareda sahibinsa syd Aliyu harazimi, akayi abinda akayi acan
Daganan ne yazama kudbul makhtoom.. Saboda haka shehu ke cewa munada muqami wanda babu wanda yasanshi sai Allah, da zamu bude da manyan rijalai sun karyatamu, wasuma kafirtamu zasuyi
Daganan ya halifantarda syd Aliyu harazimi muqamul hidmati wato Qudbaniyya
Sayyidu aliyul harazimi shi yafara zama a wannan muqamin, dagashi sai syd Muhammad tunussee, ya kwana 7, kwana bakwai kawai yayi amma aka ganshi ya shiga gari yana ihu yana cewa bazan iya daukaba, bazan iya daukaba, ahaka harya mutu
Bayanshi sai babban namiji wato syd Aliyul Tamasini, dominshi saida ya shekara 30.

TARIHIN HARKAR MUSULUNCI KARKASHIN SHEKH IBRAHIM ZAKZAKY

TARIHI

Harkar Musulunci karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim Zakzaky ta tsiro ne tun kafin cin nasarar juyin juya hali na kasar Iran, watau tun lokacin shi Sheikh din yana dan makaranta a jami'ar Ahmadu Bello ta Zaria. Sai dai a hankali ne harkar ta rika daukan siffa yayin da su yan uwa na harkar suke kara yawa kuma suke kara samun tarbiyya da ilmi na addinin musulunci. Daga cikin irin ayyukan tarbiyya da harkar ta dauka akwai irin su karantarwa da ake kira Ta'alim,Ijtima, Daura,Ribat...

code:100029
2008/5/5  23:22
TA'ALIM
Wannan wani dandali ne na karantarwa da ake yi mafi yawa a masallatai na unguwowi daban daban na garuruwan da yanuwa din suke. Akan sa rana guda ne ko biyu gwargwadon yadda zai zama daidai da zarafin su yan uwa din inda ake taruwa maza da mata tare da jagorancin wakilin wannan gari inda za'a karanta hadisai da ayoyi na tarbiyyar dabi'u da ruhi don kara samun kusanci da Allah tabaraka wa ta'ala. Baya ga wannan ta'alim na kowa da kowa kuma kawai wani na daban wanda mafi yawa ake yi tsakanin wasu zababbu daga cikin yan uwa don karantarwa ta musamman ta yadda su wadannan yan uwa sun kasance sun fi sauran fadin ilmi da fahimta da dai sauransu.
IJTIMAH
Wannan ma wani bangare ne na ayyukan da aka sa agaba a harkan domin ganin an inganta tarbiyyan yanuwa koda yake ita ijtimah ta kasance tun a farko-farkon kafuwan harkan inda ake taruwa a daya daga masallatan jummu'a na garuruwan Kano da Zaria domin gudanar da manyan ijtima'oi ko kuma masallatan jummu'a na garuruwa daban daban don gudanar da kananan ijtimao'i. Daga baya bayan da harakr ta kara bunkasa sai ya zamana wannan nauin tarbiyyar ba zai yiwu ba saboda dalilai masu yawa ciki har da yawan jama'a don haka sai aka koma yin "Daura" maimakon ijtimah.
DAURA
Kamar yadda muka ambata a sama "Daura" ce ta maye gurbin ijtimah bayan da matsayin ijtimah din ya zama ba mai yiwuwa ba. Yadda aka saba gudanar da wannan abu kuwa shine ta hanyar shirya jawabai na malamai tare da mauduai daban daban da suka shafi tunani watau kyautata fikra kyautata dabi'au gayaran ruhi da dai sauran su wanda ake yi da manufar budawa yanuwa hanyar gyaran kai na tsawon kimanin kwanaki kamar bakwai watau sati daya. Mafi yawa a karshen ko wacce daura akan rufe ne tare da jawabin  jagoran harkan Mallam Ibrahim Zakzaky. Galibi wannan daura kan banbanta da Mu'tamar wanda ake gabatar da shi ta hanyar gayyatan sauran musulmi na gari kowa da kowa kuma galbi yakan fi yawan jama'a.
MU'TAMAR
Kamar yadda muka ambata wannan shima wata hanya ce ta haduwan yanuwa da kuma bayar da tarbiyya domin akan hadu ne a daya daga cikin dakunan taro na zamani ko daya daga cikin masallatai na gari don gudanar da shi. Inda ake gayyatar Malamai daga bangarori daban na kasar don gabatar da laccocin su akan mauduai daban daban don kyautata tarbiyyar juna. Shima a mafi yawan lokutta ana rufewa ne tare da jawabin jagoran harkar Mallam Ibrahim Zakzaky.
WA'AZOZIN RANAKUN JUMMA'A
Wa'azozin ranakun jummu'a na daya daga cikin manyan ayyukan wannan harkar inda ake samun haduwa da jama'ar musulmi a garuruwan daban daban don bijirar da matsaloli na duniya da kuma musamman ma abin da yake damun musulmi a wannan lokacin saboda samun karin haske kan abin da kuma shiray tunanin musulmi din don ingantacciyar mafihimta game da yanayi da kuma siyasar dake cikin irin wannan abu. Haka nan kuma ta wannan hanya ana samun yin magana kan al'amurran da suke bijirowa kamar irin su lokutan watannin azumi, Hajj, da dai sauran watanni na ibada na musulmi, don karin haske kan irin abin da suka doru akan al'ummar musulmi na farilla da mustahabbai.
Babu shakka a wasu masallatai da ya zamana ba zai yiwu a aiwatar da wannan abu kafin huduba ba ana samu ne a aiwatar bayan salla jumma'a kafin mutane su watse su nufi gidajen su.
BUKUKUWA DA RANAKUN JUYAYI.
Daga cikin abin da yanuwa suka sa a gaba akwai tunawa da ranakun farin ciki da kuma na bakin ciki watau bukukuwa da kuma juyayi na munasabobin ma'asumai da magabata don yin nazari kan rayuwarsu mai albarka da kuma daukan darasi a cikin rayuwar mu ta yau da kullum. Shima wannan wasu lokuta ana yin su ne ta hanyar wakilan wannan harka din a garuruwa daban daban ko kuam ta jagoran hakar Mallam Ibrahim Zakzaky. Cikin irin ranakun da ake gabatar bukukuwa don tunawa da su akwai kamar su ranar 17 ga watan Rabiul Awwal watau ranar haihuwar fiyayyen halitta Manzon Allah[SAWA], 15 ga watan Sha'aban watau daidai da ranar da aka haifi Sahibuzzaman Imam Mahdi[AS], ranar haihuwar sauran a'imma da dai sauran bayin Allah na gargaru.  Ranakun juyayi sun hada da ranar wafatin Manzon Allah[SAWA], ranar shahadar Imam Hussain[AS] a Karbala... da dai sauransu.
MUZAHARORI
Muzaharori ko kuma jerin gwano na daya daga cikin hanyar da wannan harka ke bi saboda bayyana abu muhimmi daya shafi al'ummar musulmi kamar ranakun Qudus wanda akae gabatar da jerin gwano na gaba dayan kasar sannan kuma ko wanne gari su gabatar nasu na daban don nuna goyon baya ga al'ummar Palasdinawa da kuma yin tofin Allah ya tsine ga su haramtacciyar kasar Isra'ila kan irin ta'addancin da take tafkawa a yankin na Palasdin. Koda yake dai a mafi yawan lokaci ana kokarin gabatar da wannan muzahara ta ruwan sanyi amma lokuta da dama ana samun matsalar kawo hari daga bangaren yan sanada da jami'an tsaro. 

TAKAITACCE TARIHIN SHEKH IBRAHIM EL-ZAKZAKY (H)


Takaitaccen tarihin rayuwar jagoran harkar musulunci a Nigeria Sheikh Ibrahim Zakzaky.

2008/5/29  10:17

Rana da wajen da aka haifi Sheikh:

An haifi Sheikh ne a ranar 5 ga watan Mayu shekara ta 1953[15 ga Sha'aban 1372 AH] a garin Zaria dake cikin jihar Kaduna a Tarayyar Nigeria, kuma sunan sa Zakzaky kalma ce dake nufin 'mutumin zazzau'.

Sheikh Ibrahim Zakzaky shine dan Yaqoub shi kuma dan Aliyu shi kuwa dan Tajuddin dan Imam Hussain. Shi Imam Hussain wani bawan Allah ne daya fito daga Mali yazo garin Sokoto a lokacin Mujaddadi Sheikh Usman dan Fodio[RA] ya zauna tare da shi a matsayin almajirin sa, ta haka nema a lokacin da Shehu Usman dan Fodio[RA] ya nada Mallam Musa a matsayin Amir na lardin zazzau sai ya hada shi da Imam Hussain a matsayin mai bashi shawara. Ta haka ne a hankali-a hankali auratayya ta rika shiga tsakanin iayalen su kuma suka zama yan uwan juna ta wannan tun a farkon karni na 19.

Mahaifin Sheikh Ibrahim Zakzaky ya rasu ne tun shekara ta 1972, sai dai mahaifiyar sa har yanzun tana nan raye, Sheikh shine na biyar a wajen mahaifin su.

Karatun sa:

Sheikh Ibrahim Zakzaky ya fara karatu ne tun yana yaro karami a makarantar koyon karatun Al-kurani mai girma a makarantun Allo na al'ada kamar yadda aka saba tare da surkawa da karatun ilmin addinin musulunci wajen manyan malamai na wancan lokacin har ya zuwa lokacin da ya kai shekaru goma sha shida inda ya fara haduwa da tsarin karatu na zamani a shekara ta 1979 inda ya fara karatu a makarantar horar da malaman Arabiyya dake Zaria. Sannan daga shekara ta 1971-1975 ya shiga makarantar koyon larabci ta Kano watau School for Arabic Studies[SAS] wadda aka gina tun 1934 a matsayin makarantar koyon aikin lauya. sannan kuma daga baya ita ce ta haifar da babbar jami'ar Bayero da aka sani a yanzu. Kusan baki dayan alkalin alkalan jihohin Arewa daga wannan makaranta suka sami horon su. Saboda irin yadda Sheikh Zakzaky yake da ra'ayin fadada ilmin sa kan wasu darussa da ba'a koyarwa a wannan makaranta yasa ya gwama karatun nasa na Grade II da wasu maddoji ba tare da yayi su a baya ba kamar sanin gwamnati [Government] da ilmin tattalin arziki[Economics] inda yayi jarabawar GCE a kansu. Daga bisani Sheikh yayi jarabawa ta gaba[Advanced level GCE] akan wadannan maddojin:Government, Economics,Hausa,da kuma Islamic Studies inda ya sami kyakyawan natija wadda ta bashi damar shiga jami'a kai tsaye a shekara ta 1976 zuwa 1979 inda ya fara karatun digirin farko [B. Sc] akan sanin tattalin arziki [Economics].

Sheikh yayi musharaka cikin kungiyar dalibai ta musulmi inda ya zama fitaccen mamba a cikin makaranta da kuma  matsayin kasa baki daya inda a shekara ta 1978 ya zama babban sakataren kungiyar na kasa sannan kuma yayi zama mataimakin shugaban kungiyar bangaren harkokin kasashen waje a shekara ta 1979. Sheikh Zakzaky yana daya daga cikin wadanda suka jagoranci kare Shari'ah a lokacin da aka yi wani jerin gwano na nuna goyon baya ga Shari'ah a baki dayan kasar.

Sheikh Zakzaky bisa sha'awar da yake da ita na fadada karatun sa ya ci gaba da zuwa wajen malamai da suka hada da Malam Sani Abdulkadir, Malam Isa na Madaka, Malam Sani Na'ibi da kuma Malam Ibarhim Kakaki dukkanin su a birnin Zaria. Haka nan kuma a Kano Sheikh yayi karatu wajen Shawish Abdallah na Sagagi da Malam Nuhu limamin Yola.

Ayyukan sa:

Babban aikin da Sheikh Ibrahim Zakzaky ya sanya a gaba shine karatu da kuma yada ilmi tun yana matsayin dan makaranta har ya zuwa wannan lokacin. An mayar da koyarwan sa cikin yan littafai a harshen Hausa da Turanci wadanda aka watsa su a ko ina cikin kasar sannan da yawa daga cikin wa'azuzzukan sa a yanzu suna cikin CD na Computer da kaset-kaset na Recorder a ciki da wajen kasar. Dr. Iqbal Siddiqui ya taba siffanta Sheikh a matsayin "Kashin bayan harkar musulunci a Nigeria"  Babban manufar harkar musulunci da Sheikh yakewa jagoranci shine wayar da kan musulmi abin daya doru a kansu a matsayin su na daidaiku da kuma al'umma.

Yanzun haka harkar musulunci tana da makarantu dake karkashin ta na Primary da kuma gaba da Primary sama da dari uku wadanda suke a garuruwa daban daban dake fadin kasar. Wadannan makarantu an yi musu suna da makarantun Fudiyya. Haka kuma akwai cibiyoyi da da wuraren bincike da dama a manyan garuruwa na kasar karkashin wannan harka. Harkar ta mallaki jaridar da tafi ko wacce a kasar shiga ko ina da harsheen Hausa wadda ake kira Al-mizan. Sheikh ya sami matsala da hukumomi cikin kaki ko fararen kaya wadanda suke ganin cewa irin salon wa'azin nasa yana barazana ga mulkin su. A lokacin General Sani Abacha an kama Sheikh ne da tuhumar yana wa'azin 'babu hukuma sai ta Allah'.

A halin da ake ciki dai yanzun haka harkar musulunci karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim Zakzaky ta cika shekaru 30 tana kira kan komowa karkashin tsari na musulunci.

Tsawon tsarewar da aka yiwa Sheikh:

Sheikh Ibrahim Zakzaky ya kwashe shekaru tara a tsare a kurkuku daban-daban na kasar, daga shekara ta 1981-1984 an daure shi a kurkukun Enugu sai kuma kurkukun neman bayanai da bincike na jami'an leken asiri na kasa dake Lagos[Intorregation center] a shekara ta 1984-1985 sai kuma Kiri-kiri a shekara ta 1985 kurkukun Port harcout daga 1987-1989 sannan daga 1996-1997 duk dai a can Port Harcout. Sai kuma kurkukun Kaduna a 1987 sannan daga 1997-1998.

Tafiye-Tafiyen sa:

Sheikh Zakzaky yayi tafiya zuwa kasashe kamar su Britaniya, Saudi Arabia, Iran, Lebanon, Afrika ta kudu, Amurka, da Rasha. Dukkanin wadannan tafiye-tafiye yayi sune ta hanyar gayyata don dalilai na addini ko halartan tarurrukan karawa juna ilmi.

Mata da yara:

Sheikh yana da mace daya da kuma yaya tara.

IZALA DA TAWASSULI DA ANNABI (s.a.w.w)

HUKUNCIN YIN TAWASSILI DA ANNABI KO DARAJAN ANNABI KO WANI SALIHIN BAWA 

♥ ♥ بسم الله الرحمن الرحيم Sauda dama nakanji mutane suna addu‘ah da cewa (ya Allah ka bamu abu zaka... Don darajan annabi (saw) ko makamanci haka, Wanda hakan yasa naga ya kamata ayi ma mutane matashiya don wani ji kawai yake ana fad be san ingancin hakan ko rashinsa ba, Kai tsaye malaman muslunci sun tabbar da cewa ba‘a tawassli da wani mutum don darajansa ko matsayinsa ko fifikonsa acikin mutane koda kuwa annabin Allah (saw) kuma (hakan bai nuna annabi bashi da wani daraja ba a‘a yana dashi marar misaltuwa,) Malaman sunnah suka ce yin hakan ya sa6a koyarwan annabi (saw) Sai-dai ana iya yin tawassili da addu‘an annabi ko wani salihin bawa cikin bayin Allah (wato: in kana buQan abu awajen Allah ya halatta kaje wannan wani bawa salihi kayi kamun Qafa dashi ya maka addu‘a wanda hakan ake kira da TAWASSILI) Malaman sunnah suna kafa hujja da wasu hadisai ingantattu daga cikin akwai wannan hadisi wanda imamul bukhari ya rawaito... وعن أنس أن عمر رضي الله عنه كان إذا قحطوا استسقى بالعباس بن عبد المطلب وقال; أللهم إنا كنا نستسقى إليك (بدعاء) نبينا فتسقينا, وإنا نتوسل إليك (بدعاء) عم نبينا فاسقنا, فيسقون (ma‘ana) anas (ra) yace umar dan-khattab ya kasance in an samu fari (babu ruwan sama) sukanyi kamun Qafa da Abbas dan-abdul‘muddalib sai suce ya Allah da mu kasance muna tawissili da (addu‘an) annabin ka saika shayar damu to yanzu (tunda annabi baya nan) muna tawassili da addu‘an baffan annabinka ya Allah ka shayar damu (sai su daga hannu sama suce Abbas kayi addu‘ah su kuma suna cewa amin) Me sharhin wannan hadisi yake cewa وفى عمل عمر هذا هدم لعقيدة المبتدعة القاءلين بالتوسل بالموتى من اﻷنبياء والصلحين إلى الله, فما من شك أن عمر والصحابة كانوا يعلمون أن النبي (ص) هو أفضل الخلق عند الله حيا و ميتا, وأن مكانته عند ربه لم تنقص بالموت بل زادت, فالتوسل بالنبي (ص) إنما كان بدعاءه فى حياته لا بجاهه, كما أن التوسل بالعباس إنما بدعاءه لا بجاهه, (Ma‘ana) Yace wannan abu da sayyadina umar ya aikata yana nuna martani/raddi ne ga masu aQidar cewa ana iya tawassili da mamata cikin annabawa ko salihan bayi (wato kamun Qafa dasu zuwa ga Allah) Kuma babu shakku akan cewa umar (r.a) da sauran sahabbai duka sun san babu wani mutum me falala da daraja awajen Allah sama da annabi (saw) acikin rayuwansa dama bayan mutuwan sa. Kuma matsayin awajen ubangijinsa bai ragu ba sai dai ma Qaruwa yayi, amma duk da haka basuje kabarinsa sukayi kamun Qafa dashi ba, Kuma anan tawassli (kamun Qafa) da sukayi da annabi ana nufin da addu‘an annabi ne bada zatinsa (jahi) ba alokacinda yake raye Hakama shi abbas bada zatinsa ko (jahinsa) suka yi tawassili ba a‘a da addu‘ansa ne, Abunda mallam yake nuna mana anan shene Duk da cewa sahabbai sunsai babu mafi falala kamar annabi amma basa tawassili dashi sai-dai kawai sukai masa kukansu ya roQa musu Allah, Kuma inda ana tawassli da annabi ko wani salihin bawa a bayan mutuwansa ai da sayyadina umar beje gun abbas ya musu addu‘ah ba Tunda ga kabarin annabi acikin garin madina da saiyaje kawai, Misalan suna da yawa.
HUKUNCIN YIN TAWASSILI DA ANNABI KO DARAJAN ANNABI KO WANI SALIHIN BAWA ♥ ♥

بسم الله الرحمن الرحيم

Sauda dama nakanji mutane suna addu‘ah da cewa (ya Allah ka bamu abu zaka... Don darajan annabi (saw) ko makamanci haka,
Wanda hakan yasa naga ya kamata ayi ma mutane matashiya don wani ji kawai yake ana fad be san ingancin hakan ko rashinsa ba,

Kai tsaye malaman muslunci sun tabbar da cewa ba‘a tawassli da wani mutum don darajansa ko matsayinsa ko fifikonsa acikin mutane koda kuwa annabin Allah (saw) kuma (hakan bai nuna annabi bashi da wani daraja ba a‘a yana dashi marar misaltuwa,)

Malaman sunnah suka ce yin hakan ya sa6a koyarwan annabi (saw)
Sai-dai ana iya yin tawassili da addu‘an annabi ko wani salihin bawa cikin bayin Allah (wato: in kana buQan abu awajen Allah ya halatta kaje wannan wani bawa salihi kayi kamun Qafa dashi ya maka addu‘a wanda hakan ake kira da TAWASSILI)

Malaman sunnah suna kafa hujja da wasu hadisai ingantattu daga cikin akwai wannan hadisi wanda imamul bukhari ya rawaito...
وعن أنس أن عمر رضي الله عنه كان إذا قحطوا استسقى بالعباس بن عبد المطلب وقال; أللهم إنا كنا نستسقى إليك (بدعاء) نبينا فتسقينا, وإنا نتوسل إليك (بدعاء) عم نبينا فاسقنا, فيسقون

(ma‘ana) anas (ra) yace umar dan-khattab ya kasance in an samu fari (babu ruwan sama) sukanyi kamun Qafa da Abbas dan-abdul‘muddalib sai suce ya Allah da mu kasance muna tawissili da (addu‘an) annabin ka saika shayar damu to yanzu (tunda annabi baya nan) muna tawassili da addu‘an baffan annabinka ya Allah ka shayar damu (sai su daga hannu sama suce Abbas kayi addu‘ah su kuma suna cewa amin)

Me sharhin wannan hadisi yake cewa
وفى عمل عمر هذا هدم لعقيدة المبتدعة القاءلين بالتوسل بالموتى من اﻷنبياء والصلحين إلى الله, فما من شك أن عمر والصحابة كانوا يعلمون أن النبي (ص) هو أفضل الخلق عند الله حيا و ميتا, وأن مكانته عند ربه لم تنقص بالموت بل زادت,
فالتوسل بالنبي (ص) إنما كان بدعاءه فى حياته لا بجاهه, كما أن التوسل بالعباس إنما بدعاءه لا بجاهه,
(Ma‘ana)
Yace
wannan abu da sayyadina umar ya aikata yana nuna martani/raddi ne ga masu aQidar cewa ana iya tawassili da mamata cikin annabawa ko salihan bayi (wato kamun Qafa dasu zuwa ga Allah)
Kuma babu shakku akan cewa umar (r.a) da sauran sahabbai duka sun san babu wani mutum me falala da daraja awajen Allah sama da annabi (saw) acikin rayuwansa dama bayan mutuwan sa.
Kuma matsayin awajen ubangijinsa bai ragu ba sai dai ma Qaruwa yayi, amma duk da haka basuje kabarinsa sukayi kamun Qafa dashi ba,

Kuma anan tawassli (kamun Qafa) da sukayi da annabi ana nufin da addu‘an annabi ne bada zatinsa (jahi) ba alokacinda yake raye
Hakama shi abbas bada zatinsa ko (jahinsa) suka yi tawassili ba a‘a da addu‘ansa ne,

Abunda mallam yake nuna mana anan shene
Duk da cewa sahabbai sunsai babu mafi falala kamar annabi amma basa tawassili dashi sai-dai kawai sukai masa kukansu ya roQa musu Allah,

Kuma inda ana tawassli da annabi ko wani salihin bawa a bayan mutuwansa ai da sayyadina umar beje gun abbas ya musu addu‘ah ba
Tunda ga kabarin annabi acikin garin madina da saiyaje kawai,

Misalan suna da yawa.
♥ ♥

بسم الله الرحمن الرحيم

Sauda dama nakanji mutane suna addu‘ah da cewa (ya Allah ka bamu abu zaka... Don darajan annabi (saw) ko makamanci haka,
Wanda hakan yasa naga ya kamata ayi ma mutane matashiya don wani ji kawai yake ana fad be san ingancin hakan ko rashinsa ba,

Kai tsaye malaman muslunci sun tabbar da cewa ba‘a tawassli da wani mutum don darajansa ko matsayinsa ko fifikonsa acikin mutane koda kuwa annabin Allah (saw) kuma (hakan bai nuna annabi bashi da wani daraja ba a‘a yana dashi marar misaltuwa,)

Malaman sunnah suka ce yin hakan ya sa6a koyarwan annabi (saw)
Sai-dai ana iya yin tawassili da addu‘an annabi ko wani salihin bawa cikin bayin Allah (wato: in kana buQan abu awajen Allah ya halatta kaje wannan wani bawa salihi kayi kamun Qafa dashi ya maka addu‘a wanda hakan ake kira da TAWASSILI)

Malaman sunnah suna kafa hujja da wasu hadisai ingantattu daga cikin akwai wannan hadisi wanda imamul bukhari ya rawaito...
وعن أنس أن عمر رضي الله عنه كان إذا قحطوا استسقى بالعباس بن عبد المطلب وقال; أللهم إنا كنا نستسقى إليك (بدعاء) نبينا فتسقينا, وإنا نتوسل إليك (بدعاء) عم نبينا فاسقنا, فيسقون

(ma‘ana) anas (ra) yace umar dan-khattab ya kasance in an samu fari (babu ruwan sama) sukanyi kamun Qafa da Abbas dan-abdul‘muddalib sai suce ya Allah da mu kasance muna tawissili da (addu‘an) annabin ka saika shayar damu to yanzu (tunda annabi baya nan) muna tawassili da addu‘an baffan annabinka ya Allah ka shayar damu (sai su daga hannu sama suce Abbas kayi addu‘ah su kuma suna cewa amin)

Me sharhin wannan hadisi yake cewa
وفى عمل عمر هذا هدم لعقيدة المبتدعة القاءلين بالتوسل بالموتى من اﻷنبياء والصلحين إلى الله, فما من شك أن عمر والصحابة كانوا يعلمون أن النبي (ص) هو أفضل الخلق عند الله حيا و ميتا, وأن مكانته عند ربه لم تنقص بالموت بل زادت,
فالتوسل بالنبي (ص) إنما كان بدعاءه فى حياته لا بجاهه, كما أن التوسل بالعباس إنما بدعاءه لا بجاهه,
(Ma‘ana)
Yace
wannan abu da sayyadina umar ya aikata yana nuna martani/raddi ne ga masu aQidar cewa ana iya tawassili da mamata cikin annabawa ko salihan bayi (wato kamun Qafa dasu zuwa ga Allah)
Kuma babu shakku akan cewa umar (r.a) da sauran sahabbai duka sun san babu wani mutum me falala da daraja awajen Allah sama da annabi (saw) acikin rayuwansa dama bayan mutuwan sa.
Kuma matsayin awajen ubangijinsa bai ragu ba sai dai ma Qaruwa yayi, amma duk da haka basuje kabarinsa sukayi kamun Qafa dashi ba,

Kuma anan tawassli (kamun Qafa) da sukayi da annabi ana nufin da addu‘an annabi ne bada zatinsa (jahi) ba alokacinda yake raye
Hakama shi abbas bada zatinsa ko (jahinsa) suka yi tawassili ba a‘a da addu‘ansa ne,

Abunda mallam yake nuna mana anan shene
Duk da cewa sahabbai sunsai babu mafi falala kamar annabi amma basa tawassili dashi sai-dai kawai sukai masa kukansu ya roQa musu Allah,

Kuma inda ana tawassli da annabi ko wani salihin bawa a bayan mutuwansa ai da sayyadina umar beje gun abbas ya musu addu‘ah ba
Tunda ga kabarin annabi acikin garin madina da saiyaje kawai,

Misalan suna da yawa.

AN KAFA KUNGIYAR IZALA NE DON...

AN KAFA KUNGIYAR IZALAH NE SABODA KAUDA BIDI'AH DA KUMA TSAIDA SUNNAR ANNABI MAI TSIRA DA AMINCIN ALLAH


AN KAFA KUNGIYAR IZALAH NE SABODA KAUDA BIDI'AH DA KUMA TSAIDA SUNNAR ANNABI MAI TSIRA DA AMINCIN ALLAH
27/3/2013

'Yan'uwa Musulmi masu kaunar Sunnah! Muna kara tunatar da ku cewa lalle an kafa Kungiyar Jama'atu Izalatil Bid'iah Wa Iqamatis Sunnah ne a 1978 saboda a kauda dukkan wata bidiah da aka cusa cikin addinin Musulunci da sunan neman wata fa'ida a wurin Allah, sannan kuma a tsaida sunnar Annabi mai tsira da aminci cikin dukkan Aqiidah, da dukkan Ibaadah, da dukkan Mu'aamalah. Wannan shi ne dalilin kafa Kungiyar Izalah, kuma wannan ita ce manufar Izalah.

Saboda haka duk mutumin da ya ce an kafa kungiyar izala ne saboda kare wata mazhaba daga cikin mazhabobi, ko saboda kare muradun wani mutum daga cikin mutane, to lalle wannan mutum bai fadi gaskiya ba, lalle wannan mutum ya shara wa Kungiyar Izala karya, lalle wannan mutum ya ci amanar mutanen da suka hadu suka kafa wannan Kungiya tamu mai albarka.

Kuna iya fahimtar cewa duk wata mazhaba da ta saba wa nassin hadithin Manzon Allah, ko ta saba wa wani zahirin hadithin manzon Allah, cikin wata mas'ala daga cikin mas'aloli, to babu ruwan Kungiyar izala da bin wannan mazhabar cikin wannan mas'alar, a'a abin da Kungiyar Izala take yi shi ne: Sai ta bi nassin wannan hadithin, ko zahirin wannan hadithin ta bar abin da wancan mazhabar ta fada, saboda imanin da kungiyar take da shi na cewa ba a aiko mana da kowa ba cikin maluman wadannan mazhabobi, a'a wanda kawai Allah Ya aiko mana a matsayin Manzo shi ne: Annabi Muhammad mai tsira da amincin Allah.

Ga misali daya tak zan ba ku a wannan darasi namu: Tun da aka kafa wannan Kungiya tamu ta Izala, kungiyar take ta yin yaki da daura layu da guraye, kuma take ta bayyana wa al'ummar Duniya cewa daura laya shirka ce, hujjarta kuwa a kan wannan magana nata ita ce: Hadithan Manzon Allah da suka inganta cikin wannan mas'alar, kamar hadithin:-
((من تعلق تميمة فقد اشرك)).
Ma'ana: ((Duk wanda ya rataya laya to hakika ya yi ahirka)). Intaha.
A nana Annabi bai banbanta tsakanin layar da Alkur'ani ko wani ambaton Allah yake cikinta da kuma wacce babu wannan a cikinta ba, saboda haka Kungiyar izala ta yi aiki da umumi ta haramta dukkan abin da za a kira Laya.

Da luma hadithin:-
((ان الرقى والتمائم والتولة شرك)).
Ma'ana: ((Lalle Tawaida-tawaida, da kuma Layu, da Abubuwan sanya soyayya ko kiyayya tsakanin namiji da mace, shika ne)). Intaha.

Kungiyar Izala ta ci gaba da yakar layu dare da rana duk kuwa da cewa a mazhabar Malkiyyah halal ne mutum ya daura laya ko gurun da yake dauke da wasu ayoyin Alkur'ani ko kuma wasu kalmomi na ambaton Allah, kamar yadda ya zo cikin littattafan fikhun Malikiyyah kamar haka:-
1. Ya zo cikin Alfawaakihud Dawaanii sharhin Risalah t1/340 kamar haka:-
((ولا باس بالمعاذة وفيها القران)) 
Ma'ana: ((Babu laifi a daura layar da Alkur'ani yake cikinta)). Intaha.
2. Ya zo cikin Jawaahirul Ikliil sharhin Mukhtasar 1/21 kamar haka:-
((وحرز بساتر وان لحائض)).
Ma'ana: ((Layar da baduku ya rufa ta da fata halal ne a rataya ta, koda kuwa mace ce mai haila)). Intaha.
3. Ya zo cikin As'halul Madaarik kamar haka:-
((يجوز تعليق التمائم وهي العوذة التي تعلق على المريض والصبيان وفيها القران وذكر الله تعالى اذا خرز عليها جلد ويجوز تعليقها على المريض والصحيح خوفا من المرض والعين)).
Ma'ana: ((Yana halatta rataye layu, watau abin tsarin da ake rataya wa mara lafiya da kuma yara, alhali akwai Alkur'ani ko ambaton Allah Madaukaki a cikinsu, matukar dai an rufa layun da fata. Kuma rataya su na halatta ga mara lafiya, da ma wanda yake mai lafiya ne, saboda tsoron kada ya kamu da rashin lafiya ko kambun baka)). Intaha.

'Yan'uwa Musulmi masu kaunar Sunnah! Wannan ita ce Kungiyar Izala, sam ba ta barin abin da ya tabbata a cikin sunnar Annabi mai tsira da amincin, sannan ta koma ta yi riko da fatawar wata mazhaba daga cikin mazhabobi. 
Kuma Wannan shi zai tabbatar muku da cewa: Dukkan mutumin da za ku ji shi yana kyamar sahihiyar sunnar Manzon Allah cikin wata mas'ala yana cewa mu malikiyyah ne saboda haka mu abin da yake rubuce cikin mazhabar malkiyyah kadai za mu bi, domin ai su ma maluman Malikiyyan sun san da wancan hadithin amma kuma suka ki bin shi, saboda haka mu ma a nan da su za mu yi ko yi domin su ma ai magabata ne!! 
Lalle duk wanda kuka ji yana irin wadannan maganganu na shakiyanci da rashin mutunta sunnar Annabi, to lalle ku tabbatar da cewa ba dan izala ba ne na gaskiya, lalle ku tabbatar da cewa shi wannan shakiyyin mutum ya ci amanar Kungiyar Izala.

Muna rokon Allah Madaukakin Sarki da Ya tabbatar da dugaduganmu a kan sunnar Annabi mai tsira da aminci. Ame

KUNGIYAR IZALA CE TA DAWO DA RUHIN ADDINI A ZUKATAN AL'UMMAR NAJERIYA (



KUNGIYAR IZALA CE TA DAWO DA RUHIN ADDINI A ZUKATAN AL'UMMAR NAJERIYA (1)
Daga Yasir Ramadan Gwale, Kano State.
Kungiyar Jama'atu Izalatul Bid'ah Wa'Iqamatus Sunnah, kungiya ce da aka kafata domin kawar da dukkan bi'di'o'in da aka jinginawa addinin Musulunci tare da tabbatar da cikakkiyar koyarwa Addinin Musulunci a bisa tsarin koyarwar Al-Qur'ani da Hadisan Manzon Allah Salallahu Alaihi Wasallam Ingatattu, da kuma fahimtar magabata na kwarai. Kungiyar Izala kungiya ce da ta kunshi hazikan Malamai wadan da suka karantu suka san Addinin Musulunci kamar Yadda Manzon Allah Ya zo da shi.
Kusan wannan kungiya mai albarka ta kafu ne karkashin Jagorancin marigayi Shiekh Abubakar Mahmoud Gumi (Rahimahullah).­ Da Wasu Malamai da Shuwagabanni.
Sheikh Gumi yayi ta fadi tashin ganin an koyar da al'umma addinin Musulunci na hakika ba wai a Najeriya kadai ba a kusan daukacin kasashen yammacin Afurka. Cikin ikon Allah tare da taimakonsa ne Shiekh Gumi da'awarsa tayi nasara sosai, ya bayar da fatawoyin da suka fitar da al'ummar Musulmi daga duhun Jahilci da saita su akan hanya mikakkiya ta kitabu da Sunnah.
Sanin kowa ne cewar kafin bayyanar Izala, al'ummar Musulmi musamman na Arewacin Najeriya sun tasirantu da ayyukan addini da suka saba da hakikanin koyarwar Al'qur'ani da Hadisai Ingatattu. Wannan ce ta sanya dole kungiyar ta samu tirjiya daga mutanan da suka jima suna aikata Bidi'ah wanda suke zaton Addini suke yi. A karon farko anki yadda a fahimci hakikanin abinda IZALA ta zo da shi da gangan da ganganci, dan wadan da suka fahimci hakikanin abinda Izala ta zo da shi sun san cewa idan har al'ummar Musulmi suka fahimci koyarwar addini ta hakika karkashin Izala to la shakka kashinsu ya bushe kuma kasuwarsu ta kare, wannan ce ta sanya suka kasa zaune suka kasa tsaye wajen kira ga magoya bayansu kada su kuskura su saurari Malaman Izala, rahotanni sun nuna cewa wasu malaman sukan fadawa Mabiyansu cewa duk inda kaga Dan Izala yana wa'azi gwargwadon gudunka da shi gwargwadon ladan da zaka samu! Allahu akbar.
A gari irin kano wanda yake ciki da manyan Shehunnan dariqun sufaye kungiyar Izala ta fuskanci tirjiya mai girman gaske. A wasu lokuta ankai ruwa rana sosai tsakanin Malaman Izala masu wa'azi da al'ummar unguwanni da suke ganin babu dalilin da zai sanya a kyale su suyi wa'azi. Domin a lokacin anyi ta gayawa mutane karairayin cewa 'Yan Izala wasu mutane ne masu Gemu da dagaggen wando da suke Zagin Iyayan Manzon Allah (Wal'Iyazubilla­h). Wannan ta sanya Malaman Izala suka sha bakar wahala kafin samun damar fara yin wa'azi a cikin unguwannin Birnin Kano da kewaye.
Kasancewar KANO gari mafi yawan jama'a a fadin Arewa, kuma al'umma masu matukar kaunar duk wani abu da ya shafi addini, ya sanya Kano ta zama wani muhimman filin daga ga kungiyar Izala. Unguwanni irinsu Fagge Masallacin Triumph da irinsu Burged da jami'ar Bayero suna daga cikin guraran farko da suka fara cin gajiyar koyarwar Izala a jihar Kano. Amma unguwannain cikin birni an samu tirjiya mai girman gaske, takai jallin da an daddaki wasu Ustazai an sassari wasu da adduna an farfasa musu lasifikoki kai abin har ya kai da kona tare da yin kashi a cikin Masallaci a cikin birnin Kano. Masallacin 'Yan Rariya dake filin Mushe a Karamar Hukumar Gwale yana daga cikin masallatan Izala na farko farko a cikin birnin Kano, an shafe lokaci mai tsawo ana yin kashi da zuba shara a cikin masallacin, laifinsu kawai shine sunyi Sallar Azahar karfe daya na Rana!
Haka kuma, idan muka kalli Jami'ar Bayero kusan nanne inda Izala bata samu wata tirjiya ba wajen yin wa'azi. Wannan kuwa baya rasa nasaba da cewa Dalibai da malamai na Jami'ah suna da cikakkiyar wayewa ta fahimtar rayuwa da fahimtar inda duniya ta sanya a gaba, dan haka ne Masallacin Jami'ar ya zama wani dandalin Izala a cikin kwaryar birnin Kano. Masu magana sukance Duniya Labari, yanzu Izala har a tsakiyar Tudun Nufawa da Makwarari da Madabo da Kofar Wambai da sauran unguwanni na cikin birnin Kano.
Wannan ne dalilin da ya sanya wasu daga cikin Malaman da suke ganin Izala matsala ce a garesu idan har al'umma suka fahimce su suka fara saduda tare da zubawa sarautar Allah ido. Amma kuma dole wasu suka tashi haikan wajen bincike da Nazarin Ilimin addinin Musulunci, domin tsira da mutunci dan kada mutanan da sukewa kallon yara matasa su ringa kuresu tare da tsiraita iliminsu.
Bayan kafuwar Izala, ta assasa WA'AZIN KASA wanda ake hada kafatanin Malaman da suke Izala a wata jiha domin yin wa'azi tare da kira zuwa ga Al-Qur'ani da Sunnah. Wannan wa'azi da Izala take yi yayi tasiri kwarai da gaske wajen janyo hankulan mutane, tare kuma da sanya 'yan uwantaka ta addini a tsakanin Ustazai. Wani abin sha'awa shine a duk lokacin da Izala ta shiga wata Jiha domin yin wa'azi to shakka babu mutanan wajen da za'ayi wa'azin sukan samu habakar tattalin arziki, domin masu kankanan sana'o'i kanyi ciniki sosai na hajojinsu, a filin wa'azi wani Ustazu zai zo ya karkace ya kirawo Me Ganda ya saye daron gaba daya yace a yankawa jama'a suci su sha romo, wannan ko shakka babu ya kara karfin 'yan uwantaka ta addini a tsakanin Matasa.
Yasir Ramadan Gwale
07-06-2013

TARIHIN SHEKH MAHMUD GUMI

An haifi Shaikh Abubakar Mahmud Gumi (R.A) ne a cikin garin Gumi a Jahar Sakkwato a Arewacin Nijeriya, a shekara ta 1340 bayan Hijira dai dai da shekarar Miladiyya 1922.

Mallam ya tashi ne cikin kyakkyawar tarbiyya da natsuwa da tsafta da neman Ilimi karkashin kulawar mahaifin sa (Alkalin Gumi a wancan zamanin). Kuma yayi karance-karance na zaure a majalisi daban-daban na Malaman da suka shahara anan kasar Hausa a wancan lokaci, tare da karatu na nizamiyya daga nan kasar har kasar Sudan da kasar Saudi Arabiya.

Shaikh Abubakar Gumi mutum ne mai kokarin binciken Al-kurani da Sunna kan hukunce-hukuncen Shari’a, tun daga abin daya shafi Tauhidi, Hadisi, Fikhu da luggar Larabci, wanda karantarwar da yayi ta tabbatar da haka.

Muna fatan Allah (SWT) cikin Rahamar Sa yayi gafara da jin kai da daukaka ga wannan bawa na sa, wanda ya jaddada Da’wah ta Sunna a wannan kasa mai albarka, tun bayan wafatin Shaikh Usman Dan Fodio (RH).

TARIHIN SHEHU IBRAHIM INYASS

TARIHIN SHEHU IBRAHIM INYASS



Tarinhin shehul-islam sheikh ibrahim inyass

Shine sheikh ibrahim dan shehu Adullahi Inyass. An Haifeshi Agarin (daiban yasin) gari ne da mahaifinsa yakafa a kaulakh dake kasar senegal. Ranar alhamis Bayan la`asar 15 rajab ,1900. Hijra 1320.
Yatashi akan kularwar mahaifinsa, ya Haddace Al-Qur'ani a Hannun mahaifinsa Acikin kananan shekaru Ya wallafa littafi A rana daya yana da shekaru 21 aduniya. Ya turo ilimi Zahiri dana Badini Har Yazama baida Tamka a Fagen ilimi a duk duniya. Yazama Gagara Misali acikin son Manzo Allah (SAN) da yabonsa. Faiyar da Shehu Ahmadu Tijjani mai Darika yai Bushara da Zuwanta ta Bayyana a Hannunsa a HiJra 1348.

Yayi HIJra daga garinsu Kaulaka Ranar Safiyar Sallah 1939. Yatafi HaJJin Farko 1937 kuma a wannan shekara ce ya hadin da sarkin kano shehu Abdullahi Bayaro (sarkin AlhaJi) wanda yai Asalin shigowar shehu Nigeria
Shehu yai wallafa littafai Ba’ adadi daga cikin akwai, shahararren Duwaninsa da Kashiful ILbas da Ruhul –Adat . Yaba″YAya 75 MAZA da MATA ya rayu shekaru 75 yarasu A Asibitin London Rana 15 ga Rajab.An rufeshi A Madinarsa a Gaban Masallacinsa Raularsa ta Zama Abin Ziyara a Kowa ne Lokaci

A na Masa Lakabi da

Shehul Islam

Abu Ishaq

Sahibul Faidha

Inyass.

Allah yakaramashi Karama Amin

DON KARIN BAYANI A ZIYZRCI WWW.AL-FATIMIYYA.ORG

TARIHIN SHEKH JA'AFAR

Tarihin Sheikh Jafar Mahmud
Adam***
An haifi marigayi Sheikh
Ja'afar Mahmoud Adam a
garin Daura, a shekara ta 1962
(ko da yake wani lokacin
yakan ce 1964).
Marigayi Sheikh Ja'afar ya fara
karatunsa na allo a gidansu, a
wurin mijin yayarsa, Malam
Haruna, wanda kuma dan
uwansu ne na jini. Daga nan
kuma sai aka mayar da shi
wajen wani Malam Umaru a
wani gari wai shi Koza,
kimanin kilomita 9 a arewa da
Daura, wanda shi ma akwai
dangantaka ta jini a tsakanin
su, wanda kuma shi ne
musabbabin zuwansa Kano.
Bayan sun zo Kano ne tare da
wannan malami nasa, a
shekara ta 1971 (ko 1972), sai
suka zauna a makarantar
Malam Abdullahi, wanda
asalinsa mutumin jamhuriyar
Nijar ne, amma yake zaune a
unguwar Fagge a Kano. Tun
kafin zuwansu Kano, tuni
marigayi Sheikh Ja'afar ya riga
ya fara haddar Alkur'ani mai
girma, wanda ya kammala a
shekara ta 1978.
Bayan da Malam ya kammala
haddar Alkur'ani mai girma,
kasancewarsa mai sha'awar
ilimi, sai ya shiga makarantu
biyu a lokaci daya a shekara
ta 1980. Ya shiga makarantar
koyon Larabci ta mutanen
kasar Misra a cibiyar yada
al'adun kasar Misra, (Egyptian
Cultural Centre), sannan
kuma ya shiga makarantar
manya da ba su yi boko ba ta
Masallaci Adult Evening
Classes, tunda a lokacin
shekarunsa sun wuce shekaru
na primary, amma duk da
haka a wannan lokaci shi ne
mafi kankanta a ajinsu. Haka
ya rika yin wannan karatu
guda biyu: Waccan
makarantar ya je ta da
daddare bayan sallar isha'i,
waccan kuma ta koyo harshen
larabcin da yamma. Ya
kammala wadannan
makarantu a shekara ta 1983.
Wannan kuma shi ya ba shi
damar shiga makarantar
GATC Gwale a shekara ta
1984, kuma ya kammala a
shekara ta 1988. A shekara ta
1989, malam ya sami gurbin
karatu a jami'ar musulunci ta
Madinah, a inda ya karanta
ilimin tafsiri da Ulumul Kur'an,
wanda kuma ya kammala a
shekara ta 1993. Sannan kuma
Sheikh Ja’afar ya sami damar
kammala karatunsa na digiri
na biyu (Masters) a Jami’ar
Kasa-Da-Kasa Ta Afrika da
take Khartoum, Sudan.
Sannan kuma, kafin
rasuwarsa, ya riga ya yi nisa
wajen karatunsa na digiri na
uku, wato digiri da digirgir
(PhD), a Jami’ar Usman Dan
Fodiyo da take Sokoto.
Daga cikin malamansa na
ilimi, akwai malaminsa na
farko, mutumin kasar Masar,
Sheikh Abdul-Aziz Ali al-
Mustafa, da kuma Malam
Nuhu a unguwar Dandago,
wanda malam ya karanci ilimi
fikihun malikiyya da wadansu
littattafai na hadisi a gurinsa,
da kuma Malam Muhammad
Shehu, mutumin Lokoja,
wanda Malam ya karanci
nahawu da sarfu da balaga da
adab a wajensa. Akwai kuma
Sheikh Abubakar Jibrin
limamin masallacin Juma'a na
BUK, akwai kuma Dr. Ahmad
Muhammad Ibrahim shi ma na
jami'ar Bayero ta Kano. Daga
cikin malamansa na jami'a
kuma, akwai Sheikh
Abdurrafi'u da Dr. Khalid
Assabt.
Daga cikin karatuttukan da
malam ya karantar da su, sun
hada da tafsirin Alkur'ani mai
girma, Kitabuttauhiid,
Umdatul Ahkaam, Arba'una
Hadiith, Kashfusshubuhaat,
Bulugul Maraam,
Riyaadussalihiin, Siiratun
Nabawiy, Ahkaamul Janaa'iz,
Siffatus Salaatun Nabiiy.
Wasu daga cikin daliban
malam sun hada da Malam
Rabi'u Umar R/Lemo da
Malam Sani Abdullahi
Alhamidi Dorayi da Malam
Abdullah Usman G/Kaya da
Malam Usman Sani Haruna da
Malam Ibrahim Abdullahi Sani
da Malam Ali Yunus
Muhammad da Dr. Salisu
Shehu da Malam Shehu
Hamisu Kura da Malam Anas
Muhammad Madabo.
Kafin rasuwarsa, malam ya
fara gagarumin aikin rubuce
tafsirinsa a harshen Hausa a
karkashin wannan cibiya
(Sheikh Ja'afar Islamic
Documentation Centre).
Marigayi Sheikh Ja'afar
Mahmoud Adam ya rasu ranar
juma'a 26/Rabii'u Awwal/1428
(13/04/2007) sakamakon harin
da wadansu 'yan ta'adda suka
kai masa, a daidai lokacin da
yake jagorantar sallar asuba a
masallacin Juma'a na Dorayi.
Ya rasu ya bar mata biyu, da
'yaya shida, yayin da aka haifa
masa ta bakwai kwanaki 58
daidai bayan aiwatar da
wannan kisan gilla a kansa.
Dubun-dubatar mutane ne
daga ko'ina cikin kasar nan
suka halarci jana'izarsa, kuma
an binne shi ne a makabartar
Dorayi. Allah ya ji kan sa ya
gafarta masa, ya saka masa
da gidan aljanna. Amin

MANUFAR KUNGIYAR JAMA'ATU IZALATIL BIDI'AH WA IQAMATIS SUNNAH (JIBWIS).



MANUFAR KUNGIYAR JAMA'ATU IZALATIL BIDI'AH WA IQAMATIS SUNNAH (JIBWIS).
Kungiyar kawar da Bidi’ah da tsayar da sunna
Wannan qungiya ta al’ummar musulmi an kafa ta ne tun a shekarar 1978 a Najeriya, kuma shugabanta na farko shi ne Alhai Musa Gandu Muhammad, a qarqashin kulawar Malam Abubakar Mahmud Gumi, tare da Sheikh Isma’il Idris bn Zakariyya, a matsayin shugaban majalisar malamai na farko na kungiyar.
Qungiyar ita ce irinta ta farko a tarihin yada addinin musulunci a Najeriya, hadi da harkar ilmantarwa, tare da daukaka darajar harkokin addinin Musulunci ba tare da wani tsoro ba. Don haka ne sai kungiyar ta sanya wasu ginshiqan manufofi da take so ta cimma domin kai wa ga gaci.
Daga cikin muhimman manufofin wannan kungiya sun hada da:
- Kawar da duhun jahilci daga cikin al’umma, wanda ya yi wa al’umma katutu.
- Hada kan al’ummar musulmi a bisa koyarwar Alqur’ani da Sunnar Manzon Allah (SAW),
- Wayar da kan al’ummar musulmi game da al’amuran addini, domin a gudu tare a tsira tare.
- Fadakar da al’ummar musulmi domin a yi watsi da wasu miyagun littattafai da suke tura mutane cikin halaka.
- Tabbatarwa da cewa Annabi (SAW) ya kammala isar da sakon Allah (SWT).
- Duk wanda ya yi da’awar annabta, ko kuma yake riya cewa Annabi (SAW) yana ziyartarsa da wani sako, to wannan zunzurutun makaryaci ne.
- Yada Musulunci a Najeriya da wajen Najeriya.
- Yin da’awa a kan fadin Manzon Allah (SAW) cewa: “duk wanda ya ga abin qi, to ya sauya shi da hannunsa, idan ba zai iya ba, to da harshensa, in ba zai iya ba, to da zuciyarsa, amma wannan shi ne mafi raunin imani.”
- Kar a boye hujja in dai har ta tabbata daga littafin Allah Madaukakin Sarki, ko sunnar Manzon Allah (SAW).
Wasu daga cikin ayyukan kungiyar sun hada da:
Kasancewar wannan kungiya ta shahara sosai a kasashe daban-daban na duniya, wannan ya sa aka samar da kwamitoci daban-daban domin gabatar da ayyuka da yawa. Wasu daga cikin kwamitocin kungiyar sun hada da:
- Kwamitin Da’awah.
- Kwamitin Tarurrukan Wa’azi.
- Kwamitin Kula da Marayu
- Kwamitin Ilimi.
- Kwamitin Mutane Goma.
- Kwamitin Taimakon Gaggawa.
KWAMITIN ZARTASWA
Shugabanta na kasa a wannan lokaci shi ne Sheikh Abdullahi Bala Lau, khalifa na farko a sashin shugabancin wannan kungiya tun bayan kafa kungiyar, wanda tsohon mataimakin shugaban kungiyar ne a zamanin shugabancin marigayi Alh. Musa maigandu Muhammad, kuma ya gaje shugabancin kungiyar ne bayan rasuwarsa.
- Marafan Tambuwal Shine: Mataimakin Shugaban Kungiya Na Kasa.
- Sheikh Muhammad Kabir Haruna Gombe: Babban Magatakardan kungiya
- Sheik Sani Yaya Jingir: Shugaban Majalisar Malamai na kasa
- Sheik Dr. Ibrahim Jalo Jalingo Shine: Mataimakin Shugaban Majalisar Malamai na Kasa
- Alh. Isa Waziri: Shugaban Yan Agaji na Kasa
- Engr Mustapha Imam Sitti: Mataimakin Shugaban Rundunar Yan Aagaji na kasa
kungiyar ta samu karbuwa a sassa daban-daban na duniya. A Najeriya tana da rassa a dukkanin jihohin Najeriya 36 da birnin tarayya. Haka kuma saboda irin yadda kungiyar take kokarin ilmantar da al’umma, wannan ya sa har ta sami kutsawa zuwa ga wasu kasashe, kamar su; Nijar da Mali da Sinigal da Togo da Kamaru da Cadi da Burkina da Gini, Saudi Arabia da sauransu.
Wasu daga cikin abubuwan da kungiyar ta mayar da hankali wajen yin su, sun hada da:
- Koyarwa a bisa tafarkin Manzon Allah (SAW) ba tare da bin son zuciya ko kuma yin makauniyar biyayya ga wani ba.
- Tsantsar karantar da hakikanin ilimin addinin Musulunci.
- Gabatar da wa’azin kasa a duk makwanni biyu ko uku ko hudu don tunatar da mutane abin da suka manta ko kuma lokutan da suka dace.
- Kafa makarantu domin koyar da ilimin addini da na boko, da sauran fannonin ilimi.
- Kai ziyarori gidajen marayu da gidajen yari da asibitoci, domin tallafar musulmai marasa galihu.
- Samar da taimakon gaggawa a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.
kungiyar ta samar da hamshaqan malamai a sassa wadanda suka sami daukaka ta ilimi a fadin duniya baki daya, saboda jajircewa da kokarin bin tafarkin Manzon tsira, Annabi Muhammad (SAW), sau da kafa.
Haka kuma ta ko wacce fuska tarihin izala zaizo , dogo ko gajere, ba za a taba mantawa da irin gudummar da marigayi Sheikh Abubakar Mahmud Gumi da Sheikh Isma'ila Idris Bin Zakariyya suka bada ba, da irinsu Marigayi Sheikh Ibrahim Bawa Maishinkafa, Sheikh Hudu Chikaji Zariya, Sheikh Adam Maishafi, Sheikh Abubakar Imam Ikara da Sheikh Alhaji Musa Maigandu Muhammad ba, Koda ba manufarmu zayyana sunan kowa ba, amma muna addu'a ga dukkan wadanda suka sadaukar da dukiyoyin su da kuma rayukansu akan wannan harka taci gaban addini, Allah ya saka musu da gidan Aljanna ya hada mu dasu a babban matsayi a lahira.
Haka Suma Dattawan Izala na Farko Irin su Sheikh Dr. Alhassan Sa'eed Adam jos wanda shine Alaramma na farko a tarihin kafuwar kungiyar, da Sheikh Yakubu Musa Hassan Katsina, Sheikh Usman Isah Taliyawa Gombe, Sheikh Sa'idu Hassan Jingir, Sheikh Abdullahi Bala Lau, Sheikh Sani Yahaya, Sheikh Rabi'u Aliyu Daura, Alaramma Abubakar Adam Katsina, Alaramma Yahuza Bauchi da Sauran Shuwagabanni da yan agaji, muna addu'an Allah ya saka ma kowa da alkhairi ya hada mu a gidan aljanna fir'dausi.
Wannan kadan ne daga cikin irin manufofin da kungiyar Izala ta kafu a kayi tun asali, kuma a haka za'a tafi da ikon Allah.
Muna Addu'an Allah ya karkato Mana Da Hankulan Jagororin mu a koma Karantarwan Kungiyar ta Asali, Wato Kira kan Kitabu Wassunnah.
Daga Karshe Muna Addu'an Allah ya nuna mana gaskiya gaskiya ce ya bamu ikon binta, ya nuna mana karya karya ce ya bamu ikon guje mata.